Connect with us

News

Ƴan daba sun far wa ƴan majalisar dokokin Bauchi inda su ka jikkata 6

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

A jiya Litinin ne dai wasu ɓata-gari su ka kai wa ƴan majalisar dokokin Jihar Bauchi farmaki a gidan shaƙatawarsu, inda su ka raunata mutum shida tare da lalata motoci da tagogi a gidan.

An Zabi El-Rufai Abokin Takarar Tinubu

Advertisement

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya bayar da rahoton cewa majalisar ta faɗa cikin rikicin shugabanci inda a ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne mambobi 22 su ka kaɗa ƙuri’ar rashin goyon baya ga shugaban majalisar, Abubakar Suleiman da sauran masu riƙe da muƙamai a majalisar.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Babale Abubakar, ya shaida wa manema labarai a jiya Litinin a Bauchi cewa, harin da ya faru da misalin karfe 4 na yamma, a daidai lokacin da ƴan majalisar ke gudanar da taro, ya yi sanadin jikkata shida daga cikinsu.

“Akalla motoci shida maharan suka lalata da su kuma suka fasa gilashin tagogi.

“Sun fi 100 kuma suna ɗauke da bindigogi, kokara da adduna,” in ji shi.

“Abin ban tsoro ne. Wasu daga cikin mu sun gudu zuwa kofar fita kuma sun ji rauni sosai,” in ji shugaban masu rinjaye.

“Al’amari ne mai ban tsoro. Abin bakin ciki ne,” inji sh

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending