Connect with us

News

Idan Na Zama Shugaban Kasa Yajin Aikin ASUU Zai Zama Tarihi – Kwankwaso

Published

on

 

Daga Khadija Abdullahi Mahmud 

 

 

 

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce daga ranar da ya zama Shugaban Kasa an daina yajin aikin malaman jami’o’i a Najeriya.

Advertisement

 

Kwankwaso wanda har ila yau tsohon Ministan Tsaro ne kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano ya bayyana hakan ne a wata hirar ta musamman da manema labarai a Gombe, inda ya ce da zarar an zabe shi malaman jami’a za su daina kuka.

Jirgin ruwa ya kife da mutane 20 a Legas

 

Yace in ban da harkar siyasa da ya shiga da yanzu shi Farfesa ne, inda ya ce malaman jami’a ’yan uwansa ne zai zauna da su ya saurare su.

 

Advertisement

“A siyasar ma ni ba irin wanda za a tambaya ina satifiket dinsa bane ya tsaya kame-kame ko ya ce ya bata ba ne,” inji Kwankwaso.

 

Ya kuma ce bangaren da zai bai wa fifiko shi ne na ilimi kamar duk wanda ya san Kano lokacin yana Gwamna ya san ya bar tarihi a Jihar wajen inganta fannin.

 

A cewarsa, ba zai kwashe kudin Najeriya don biya musu bukata ba, zai duba matsalar ce tun daga farko ya dakile ta, yana mai cewa ba zai kwashe kudin kasa ba, kuma ba zai bari a kwashe ba dole sai da dalilin abin da za a yi da kudin.

 

Advertisement

Yace idan ya zama Shugaban kasa, duk wani azzalumi zai kama shi ya kai gidan gyaran hali idan ya gyara halin sannan a fito da shi.

 

Daga nan sai dan takarar ya yi kira ga malaman jamio’in da su yi wa Allah da Manzonsa su koma Aji domin gwamnati ba kallon su za ta yi ba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending