News
Karancin man Fetur a Kamaru ya tilasta wa kungiyar direbobi jingine ayyukanta
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Shugaban kungiyar direbobin motocin haya a Kamaru Ibrahim Yaya, ya ce karancin man fetur ya tilasta wa ‘ya’yan kungiyar jingine ayyukansu.
A wata sanarwa da Ministan makamashin kasar ya fitar ranar Litinin ya yi alkawarin kawo man cikin ‘yan kwanaki masu zuwa.
Mista Essomba ya yi bayanin cewa karancin man ya faru ne sakakamon karuwar kudin tallafin man da gwamnati ke biya saboda tashin farashin man a kasuwar duniya.
Inda ya ce gwamnati na bukatar isasshen lokaci domin tara kudin da za ta iya biyan tallafin.
Advertisements
