News
Nasarar da Adeleke ya samu babban darasi ne ga APC — Adamu
DAGA KHADIJA ABDULLAHI MAHMUD
Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, ya ce kayen da jam’iyyar ta sha a zaben gwamnan jihar Osun a ranar 16 ga watan Yuli zai zama darasi ga jam’iyyar gabanin zaben 2023.
An Kara Farashin Fetur Daga N165 A Najeriya
DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa dan takarar jam’iyyar People’s Democratic Party, Ademola Adeleke, ya doke gwamna mai ci kuma dan takarar jam’iyyar APC, Gboyega Oyetola, a zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 16 ga watan Yuli.
Da yake magana a wata hira da Sashen Hausa na BBC, Mista Adamu ya ce bayan shan kayen da aka yi, ya bayyana cewa akwai rikici a jam’iyyar.
Don haka Adamu ya yi kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ka ji haushin su da su zage damtse domin ganin jam’iyyar ta samu nasara a zaben 2023 mai zuwa.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
