Connect with us

Sports

Kashi 60 Zuwa 80 Na ‘Yan Kallo Za A Bari Su Shiga Kallon Wasannin Gasar AFCON Saboda COVID – CAF

Published

on

8D3061B2 AD39 4D73 95C6 4820BB4865D0 w408 r1
Spread the love
  • Daga

 

  • Usman
  • Abdullahi Nguru

 

A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar COVID ta sa aka dage zuwa bana.

Hukumar Kwallon Kafa ta nahiyar Afirka CAF ta ce kashi 60 zuwa 80 na ‘yan kallo za a bari su shiga filayen wasanni da za a kara gasar cin kofin nahiyar na AFCON.

Matakin a cewar hukumar na da nasaba da annobar COVID-19.

Advertisement

Cikin wata sanarwa da ta fitar, CAF ta ce bayan wata tattaunawa da ta yi da hukumomin cikin gida na Kamaru, sun cimma matsaya akan cewa kowanne filin wasa za a bar ‘yan kallo kashi 60 ne zuwa 80 su shiga kallo.

A ranar 9 ga watan nan na Janairu za a bude gasar ta cin kofin nahiyar Afirka, wacce Kamaru ke karbar bakunci.

Za kuma a kammala a ranar 6 ga watan Fabrairu kamar yadda jadawali gasar ya nuna.

A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar COVID ta sa aka dage zuwa bana.

Advertisement

Kasar Aljeriya ce ke rike da kofin gasar.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *