Connect with us

News

DA ƊUMI-ƊUMI: Makiyaya Sun Kashe Mutane Biyar Bayan

Published

on

121755241 mediaitem121755240.jpg
Spread the love

Daga Muhammad zahraddin

 

 

Advertisement

Al’ummar Arimogija da ke karamar hukumar Ose a jihar Ondo ta shiga rudani a yammacin ranar Litinin din da ta gabata yayin da wasu ‘yan bindiga da ake zargin Fulani makiyaya ne suka kai wani sabon hari a garin, inda suka kashe mutane biyar.

Harin dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki garin Omolege da ke kan iyaka a karamar hukumar, inda suka kashe mutane uku tare da kona gidaje da dama.

An ce shugaban al’ummar na cikin wadanda aka kashe.

Advertisement

A ranar Lahadin da ta gabata ne Gwamna Rotimi Akeredolu ya ziyarci yankin karamar hukumar inda ya sha alwashin farautar wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Gwamnan ya ziyarci wurin ne tare da kwamishinan ‘yan sandan jihar Mista Oyediran Oyeyemi; Kwamandan Rundunar Amotekun, Tunji Adeleye; da wasu ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

Sai dai kuma, sa’o’i kadan bayan ziyarar, SaharaReporters ta tattaro cewa ‘yan bindigar sun kai hari a wata al’umma a karamar hukumar, inda suka kashe akalla mutane biyar.

Advertisement

Wadanda aka kashe sun hada da shugaban matasan yankin, Augustine Lucky; Osaromere Augustine; Odalume Stephen; Okpakoro da Monday Black.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *