News
Majami’a ta rufta tare da kashe mutane 10 a Delta

Daga kabiru basiru fulatan
Wani ginin gidajen majami’a na Salvation Ministry, Okpanam, a karamar hukumar Oshimili ta Arewa, a jihar Delta, a Kudu maso Kudancin Najeriya, ya ruguje, tare da danne masu ibada da ba a tantance adadinsu ba.
Politics Nigeria ta rawaito cewa, sama da mutane 10 a ka zargi sun mutu a cikin ginin.
Rahotanni na cewa, ginin da aka fara amfani da shi a karon farko, ya ruguje ne da misalin karfe 5:55 na yammacin ranar Talata.
An ceto mutane 8 ba tare da sun ji rauni ba, yayin da a ka garzaya da mutane hudu asibitin kwararru na Asaba, domin kula da lafiyarsu.