Connect with us

Sports

Najeriya ta tsayar da ranar da za ta yi karon-batta da Ghana don zuwa gasar duniya

Published

on

FB IMG 16443869956510082
Spread the love

Za a yi karon-battar, wanda zai kasance na biyu kuma na karshe a filin wasa na MKO Abiola da ke babban birnin Najeriyar, Abuja.

Za su fatata ne bayan tawagar Super Eagles din ta koma gida daga Ghana don buga zagayen farko.

Sai dai hukumar ta Najeriya ta ce har yanzu takwararta ta Ghana (GFA) ba ta tabbatar mata da ainahin ranar da za a yi karawar farko ba, a filin wasa na Cape Coast, a tsakanin ranar Laraba, 23 ga watan Maris ko Alhamis 24 ga watan na Maris.

Advertisement

Wasan da Najeriya za ta karbi bakuncin tawagar ta Black Stars zai zama wasa na 60 tsakanin kasashen biyu da aka dade ana damawa da su a nahiyar Afrika.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *