Za a yi karon-battar, wanda zai kasance na biyu kuma na karshe a filin wasa na MKO Abiola da ke babban birnin Najeriyar, Abuja.
Za su fatata ne bayan tawagar Super Eagles din ta koma gida daga Ghana don buga zagayen farko.
Sai dai hukumar ta Najeriya ta ce har yanzu takwararta ta Ghana (GFA) ba ta tabbatar mata da ainahin ranar da za a yi karawar farko ba, a filin wasa na Cape Coast, a tsakanin ranar Laraba, 23 ga watan Maris ko Alhamis 24 ga watan na Maris.
Advertisement
Wasan da Najeriya za ta karbi bakuncin tawagar ta Black Stars zai zama wasa na 60 tsakanin kasashen biyu da aka dade ana damawa da su a nahiyar Afrika.
Za a yi karon-battar, wanda zai kasance na biyu kuma na karshe a filin wasa na MKO Abiola da ke babban birnin Najeriyar, Abuja.
Za su fatata ne bayan tawagar Super Eagles din ta koma gida daga Ghana don buga zagayen farko.
Sai dai hukumar ta Najeriya ta ce har yanzu takwararta ta Ghana (GFA) ba ta tabbatar mata da ainahin ranar da za a yi karawar farko ba, a filin wasa na Cape Coast, a tsakanin ranar Laraba, 23 ga watan Maris ko Alhamis 24 ga watan na Maris.
Wasan da Najeriya za ta karbi bakuncin tawagar ta Black Stars zai zama wasa na 60 tsakanin kasashen biyu da aka dade ana damawa da su a nahiyar Afrika.