Connect with us

News

Rikicin Ukraine: Najeriya ta jaddada gargaɗi ga ‘yan ƙasar mazauna Ukraine

Published

on

nigerian embassy ukriane e1644166282863 1280x720 1
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

Hukumar kula da lamurran ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta sake jaddada kira ga ‘yan ƙasar mazauna Ukraine da su “ankare” kuma su “rage tafiye-tafiye” musamman zuwa gabashin ƙasar.

Kiran na zuwa ne yayin da ake ta nuna fargaba kan yunƙurin Rasha na afka wa maƙociyarta Ukraine, inda ta jibge dakaru 100,000 a kan iyaka.

Advertisement

Tun a ƙarshen watan Janairu ne Nigerians in Diaspora Commission ta gargaɗi ‘yan Najeriya da su kula da tsaron lafiyarsu sannan ta ba su shawara kan yadda za su tuntuɓi ofishin jakadancin ƙasar a Ukraine.

Rasha ta sha musanta batun cewa tana shirin mamaye maƙociyar tata.

Tuni Amurka ta umarci ‘yan ƙasarta da su fice daga Ukraine ɗin.

Advertisement

Social embed from twitter

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *