Connect with us

News

A shirye muke mu kwato Najeriya daga hannun APC da jam’iyyar PDP – TNM

Published

on

FB IMG 1645533133886
Spread the love

Daga yasir sani  abdullahi

 

 

Advertisement

A ranar Talata ne tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Kwankwaso, ya bayyana kafa runduna a karkashin inuwar kungiyar National Movement, inda hakan ya kara haskawa a siyasar Najeriya a zaben 2023.

A cewarsu, rundunar za ta karbi mulki daga hannun jam’iyyar All Progressives Congress a shekarar 2023.

TNM ta ce tana sane da kwakkwaran aikinta na ceto Najeriya daga wargajewa.

Advertisement

Da yake jawabi a wajen taron, wanda ya shirya taron, Kwankwaso, ya ce burinsu na hada kai ne na ceto kasar nan.

“Tun da dadewa ‘yan Najeriya suna jiran wannan rana. Abokan ƴan Najeriya da ke waje sun daɗe suna jiran wannan rana kuma lokaci ya yi yau.

“A yau, duk ‘yan Nijeriya sun taru a anan, Kudirinmu ne na ganin mun ceto al’ummarmu daga wannan mawuyacin hali.”

Advertisement

“Kungiyar ta kasa tana da mambobi a kowace karamar hukuma da wajen kasar nan,” in ji Kwankwaso..

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *