Daga yasir sani abdullahi
News
Masu kutse na buƙatar $20,000 bayan garkuwa da shafukan intanet 34 na Mozambique
Wasu da ake zargin masu kutse ta intanet ne sun ƙwace iko da shafuka 34 na ƙasar Mozambique sa’o’i bayan gwamnatin ƙasar ta ce ta daƙile irin wannan harin a ranar Litinin.
Wata ƙungiya da ake kira “Yemeni Hackers” ta bayyana cewa ita ce ta yi kutsen.
Wasu daga cikin shafukan intanet da aka yi wa kutse sun haɗa da na hukumar kiyaye afkuwar bala’i da ma’aikatar hanyoyi da ta ruwa da ma’aikatar tsaro.
Masu kutsen sun ajiye saƙo a ɗaya daga cikin shafukan da suka yi wa kutsen inda suke buƙatar a biya su kuɗin fansa cikin sa’o’i 24 kafin su saki shafin.
Suna buƙatar a biya su dala dubu 20 ta hanyar bitcoin idan ba haka ba sun ce za su wallafa bayanan sirri na ƙasar.
-
News3 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News1 day ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
