Connect with us

News

Masu kutse na buƙatar $20,000 bayan garkuwa da shafukan intanet 34 na Mozambique

Published

on

FB IMG 1645617124085
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

Wasu da ake zargin masu kutse ta intanet ne sun ƙwace iko da shafuka 34 na ƙasar Mozambique sa’o’i bayan gwamnatin ƙasar ta ce ta daƙile irin wannan harin a ranar Litinin.

Wata ƙungiya da ake kira “Yemeni Hackers” ta bayyana cewa ita ce ta yi kutsen.

Advertisement

Wasu daga cikin shafukan intanet da aka yi wa kutse sun haɗa da na hukumar kiyaye afkuwar bala’i da ma’aikatar hanyoyi da ta ruwa da ma’aikatar tsaro.

Masu kutsen sun ajiye saƙo a ɗaya daga cikin shafukan da suka yi wa kutsen inda suke buƙatar a biya su kuɗin fansa cikin sa’o’i 24 kafin su saki shafin.

Suna buƙatar a biya su dala dubu 20 ta hanyar bitcoin idan ba haka ba sun ce za su wallafa bayanan sirri na ƙasar.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *