News
YANZU-YANZU: INEC ta bayyana dan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaben Ondo

Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa ta bayyana Mista Mayokun Lawson-Alade a matsayin wanda ya lashe zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar Ondo.
A cewar INEC, Lawson-Alade na jam’iyyar All Progressives Congress ya lashe zaben ne bayan ta samu kuri’u 26,379 inda ya doke Mista Olumuyiwa Adu na jam’iyyar Peoples Democratic Party, wanda ya samu kuri’u 24,201. Inji Punch