Connect with us

News

Ganduje ya baiwa Dangote, Abdussamad, Dantata muƙami

Published

on

FB IMG 1646248653403
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Aliko Dangote, Aminu Dantata da Abdussamad Isyaku Rabiu a matsayin mambobi na kwamitin gudanarwa na Hukumar Zakka da Hubusi ta Kano.

Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

Garba ya ce Dakta Ibrahim Muazzam Maibushira, shi ne a ka naɗa a matsayin Shugaban kwamitin.

Advertisement

Sauran, a cewar Kwamishinan, sun haɗa da Dakta AbdulMutallab Ahmed a matsayin Kwamishina I sai kuma Dakta Lawi Sheikh Atiq a matsayin Kwamishina na ll a hukumar.

Sauran sun haɗa da wakilan Masarautar Kano, wakilan Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Wakilan Ma’aikatar Harkokin Addinai, sai na kasuwannin kurmi, Rimi, Kwari da Singa.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *