Connect with us

News

Yajin aikin ASUU: Mun biya malaman jami’o’i Naira Biliyan N92.7bn –Ngige

Published

on

FB IMG 1646248959423
Spread the love

Daga muslim yunus Abdullahi

 

 

Advertisement

Ministan Ƙwadago da samar da Ayyukan yi, Chris Ngige ya yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari karin haske kan tattaunawar da a ke yi tsakanin Gwamnatin Taraiya da ƙungiyar malaman jami’o’i.

A tuna cewa ASUU ta shiga yajin aikin gargadi na tsawon wata guda tun ranar 14 ga watan Fabrairu sabo da gazawar gwamnati wajen cimma yarjejeniyoyin da aka yi da ita.

Da yake yiwa manema labarai jawabi bayan kammala taron, ministan ya ce shugaban ƙasar ya gamsu da bayanin da ya yi masa.

Advertisement

Ya ce: “Za mu aiwatar da yarjejeniyar 2020 da a ka yi da ASUU,”

A cewar sa, gwamnatin tarayya ta biya Naira biliyan 40 na alawus-alawus da kuma Naira biliyan 30 domin walwalar malaman.

Ya kara da cewa an kuma biya Naira biliyan 22.7 da ga ƙarin kasafin kuɗi sannan a ka ba su alawus-alawus na 2021.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *