News
Likita na ya faɗa min cewa shekara 5 kawai zan ƙara yi a duniya — Jarumar Nollywood
Daga yasir sani abdullahi
Jarumar masana’antar fina-finai ta Nollywood, Kemi Afolabi ta baiyana cewa likitanta ya sanar da ita cewa shekara biyar kacal za ta ƙara yi a duniya ta mutu.
A wata tattaunawa da ta yi da wani dan jarida, Chude Jideonwo, jarumar ta ce tana fama da cutar jeji mai suna lupus.
A cewar ta, likitan ya ce mata cutar ba ta warke wa, sai dai ai ta shan magani har zuwa lokacin da Allah Ya yi.
Afolabi ta baiyana cewa ta kashe sama da Naira miliyan 1 a magani amma har yanzu ba ta samu sauki yadda ya kamata ba.
A cewar ta, likitan na ta yanke mata, “ki tabbata kullum kina cikin ƴan uwan ki sabo da a ƙalla za ki iya ƙara shekar biyar nan gaba,”
Tun a watan Janairu ne Afolabi ta wallafa a shafinta na kafar instagram cewa ta rubuta wasiyya kuma har ta ajiye gurin da za a binne ta a makabarta.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
