News
Tinubu ya gana da gwamnan Ebonyi, Umahi
Daga yasir sani Abdullahi
Jagoran Jami’yar APC na ƙasa a ranar Juma’a ya gana da gwamna David Umahi na jihar Ebonyi.
In za a iya tuna cewa, wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta kori Umahi tare da mataimakinsa a ranar Laraba saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Sai dai Umahi ya daukaka kara kan hukuncin.
An jiyo cewa dan takaitaccen ganawar da gwamnan ya yi da Tinubu wanda ya gudana a Abuja ranar Juma’a bazai rasa nasaba da hukuncin kotu ba da kuma rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC.
Tinubu da Umahi dai sun nuna matukar sha’awarsu ta neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki a 2023.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
