News
DA DUMI-DUMINSA| An Kadammar da Kwalejin Kiwon lafiya ta Musulunci a Ƙasar Ghana.
Daga kabiru basiru fulatan
Maigirma Mataimakin Shugaban Kasar Ghana Dr Mahmud Bawumia ya gayyaci shugaban Kungiyar Izala na duniya Ash-sheikh Dr Abdullahi Bala Lau (H) tare da Sakataren kungiyar Izala Ash-sheikh Dr Muhammad Kabir Haruna Gombe (H)
Mataimakin Shugaban Kasar ya gayyaci Malaman zuwa Kasar Ghana domin su tattauna kan abinda ya shafi cigaban addinin Musulunci a nahiyar Afirka
Sannan an gayyaci Malaman zuwa kaddamar da sabuwar makarantar koyar da aikin kiwon lafiya wandanl aka saka mata sunan Musulunci wato Islamic Nursing Training School dake Kasar Ghana
Kamar yadda zaku gani a hoto, ginin Makarantar yana da bene uku, bene na farko an saka sunan Kakan Ahlussunnah a Nigeria, Alqadiy Sheikh Abubakar Mahmud Gumi (Rahimahullah), a bene na biyu an saka sunan Sheikh Dr Kabir Haruna Gombe, a bene na uku an saka sunan Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau
Jagoran kungiyar Izala na duniya Sheikh Abdullahi Bala Lau yayi alkawarin taimakawa wajen gudanar da wannan makaranta na Musulunci, sannan za’a dinga bada tallafin karatun kyauta a makarantar ma wasu dalibai masu kwazo
Izala ikon Allah ba na mutum ba!
Yaa Allah Ka daukaka darajar Musulunci da Musulmai a duk inda suke a duniya Amin
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
