Sports
Rasha na neman damar shirya gasar cin kofin Turai a 2028
Daga kabiru basiru fulatan
Rasha ta shiga cikin sahun jerin kasashen da ke gogayyar samun izinin karbar kakuncin kofin nahiyar Turai a shekarar 2028 da kuma 2032, duk da dakatarwar da ita da aka yi mata biyo bayan mamayar da tayi a Ukraine.
A ranar Laraban nan ce dai hukumar shirya wasannin nahiryar Turai ta bayyana sunayen kasashen da suka nuna sha’awar su na karbar bakuncin gasar inda kasashen Rasha da Turkiya da Ingila da kuma Ireland ne dai za su yi gogayya wajen neman karbar bakuncin gasar na shekarar 2028.
A watan Satunba ne ake saran hukumar UEFA za ta sanar da kasar da zata amshi bakuncin gasar.
Rasha ita ce dai ta karbi bakuncin gasar kwallon kafa ta duniya a shekarar 2018 sannan aka tsaida gudanar da wasan karshe na lashe kofin zakarun nahiyar Turai a wannan shekarar a can, sai dai daga baya aka sauya saboda mamayar da ta yi a Ukraine.
Turkiya na saran karbar bakuncin gasar bayan da ta yi rashin nasara a wajen Jamus da zata amsa bakuncin gasar na shekarar 2024.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
