Connect with us

News

Rundunar sojan sama ta Najeriya ta bayyana sunayen sojojin da suka rasu a hatsarin jirgi

Published

on

Rundunar sojan sama ta Najeriya ta tabbatar cewa matuƙa jirginta biyu ne suka rasu a hatsarin da jirgin su ya yi a Jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar.

Advertisements
Advertisements

Jirgin ya faɗo ne a yammacin jiya Talata a wani sansanin sojan saman kuma duka mutum biyun da ke ciki ne suka rasu.

Advertisements

Rundunar ta bayyana sunan dakarun nata da suna Laftanal Abubakar Muhammed Alkali da Laftanal Elijah Haruna Karatu.

Advertisements
Advertisements

A yau Laraba Hafsan Sojan Sama na Najeriya Air Marshal Oladayo Amao ya kai ziyara wurin da hatsarin ya faru don jajanta wa dangin mutanen.

Kakakin rundunar, Edward Gabkwet, ya ce za su yi “nutsattsen bincike don gano abin da ya haddasa hatsarin”.

Social embed from twitter

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending