News
Karota: bamu kama kowa ba a watan azumin Ramadan
Daga maryam Bashir musa
Hukumar Karota tayi afuwa ga wadanda aka kama da laifin keta dokar hukumar a kan tituna a wannan wata mai alfarma na Ramadan.
Mai magana da yawun hukumar Nabulusi Abubakar Kofar Na’isa, ne ya bayyana haka a wata tattaunawar sa da Premier Radio da a yammacin ranar Lahadi.
Ya ce shugaban hukumar Baffa Babba Dan’agundi ne ya bada umarnin domin kyautatawa al’umma alfarmar wannan wata.
Yace amma hakan ba yana nufin ba za a kama mai laifi ba ne, sai dai hukunci ne aka dakatar, amma ana nasiha tare da bada shawara domin a kiyaye a gaba.
Kofar Na’isa, ya kuma ce sassaucin dokar bai shafi masu kasa kayan siyarwa a bakin titi da kuma wadanda ke tsayawa a guraren da aka hana tsayawa ba.
Sai dai Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa, ya ce hukumar zata cigaba da hukunta masu ababen hawan dake karya doka da zarar watan azumin Ramadan ya wuce.
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion3 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
