News
Gwamnatin Tarayya Za Ta Bai Wa Matasa Bashin Laptop
Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani sabon shiri na bai wa matasa damar samun kwamfutocin tafi-da-gidanka (Laptop) ta hanyar bashi mai sauƙin biya, domin ƙara musu damar cin gajiyar tattalin arzikin zamani.
Shirin, wanda Hukumar Bayar da Lamuni ta Ƙasa (CREDICORP) ta ƙaddamar tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙire-ƙirƙire da Tattalin Arzikin Zamani ta Tarayya, an sanya masa suna Credit for Laptops, Internet, Connectivity and Knowledge Digital Devices (C.L.I.C.K.D.).
Jihohi 17 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa — Gwamnatin Tarayya
A matakin farko, shirin zai samar da laptop 1,000 da aka haɗa a Najeriya ga waɗanda suka cancanta daga cikin mahalarta shirin horas da matasa kan fasahar zamani na Gwamnatin Tarayya, wato Three Million Technical Talent (3MTT), ta hanyar dandalin Learn2Earn.
Da yake jawabi yayin ƙaddamar da shirin a Abuja, Ministan Sadarwa, Ƙirƙire-ƙirƙire da Tattalin Arzikin Zamani, Bosun Tijani, ya ce manufar shirin ita ce tabbatar da cewa matasan Najeriya ba wai sun samu horo kan fasahar zamani kaɗai ba, har ma sun mallaki kayan aikin da za su taimaka musu wajen amfani da ilimin da suka koya.
A cewarsa, samar da damar mallakar kwamfuta ta hanyar bashi zai taimaka wa matasa wajen samun ayyukan yi, gudanar da kasuwanci ta intanet da kuma ƙara yawan masu shiga tattalin arzikin dijital na ƙasar.
-
Opinion3 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion3 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News7 days ago
An Sace Shugaban Makaranta Da Dalibai Masu Rubuta Jarabawar NECO A Kogi
