News
Wata Ta Sake Yin Batanci Ga Annabi A Maiduguri
Daga kabiru basiru fulatan
An fara zaman dar-dar a Maiduguri babban birnin Jihar Borno, bayan wasu sun fara zanga-zanga kan wata mai suna Naomi da ita ma ta zagi Annabi Muhammad (S.A.W) a shafinta na Facebook.
Daruruwan masu zanga-zangar dai sun mamaye barikin sojoji na Garrison da ke birnin da safiyar Litinin.
Sun dai kona tayoyi tare da rufe mashigar barikin, inda nan ne aka ce Naomin take zaune, inda suka bukaci sojojin su fito da ita.
Lamarin dai ya tilasta wa Kwamandan barikin ya fito ya yi wa masu zanga-zangar jawabi tare da rokon su su kwantar da hankula.
Daya daga cikin jagororin zanga-zangar, Umar Babagana, ya shaida wa Aminiya cewa matar da ta wallafa kalaman batancin tana zaune ne tare da wani soja a cikin barikin.
Ya ce, “Mun san ta a nan yankin, kuma lokacin da ta wallafa sakon, mun bukaci a kamata a hukunta ta ko mu dauki matakin da ya dace.”
Naomi dai a cikin sakon da ta wallafa ta nuna goyon bayanta ga Deborah Samuel, dalibar da aka kashe a Sakkwato bayan ita ma ta zagi Annabin, sannan ita ma ta zage shi a cikin sakon.
Sai dai sojoji da ’yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zangar kuma abubuwa sun fara daidaita, ko da yake yanzu an girke jami’an tsaro a yankin don kaucewa sake barkewar tarzoma.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
