Koriya ta Arewa ta sanar da cewa ƙarin mutun 170,000 sun kamu da cutar korona.
Yanzu haka an killace mutum 650,000 a fadin kasar.
Babban birnin kasar Pyongyang ne ya fi fuskantar bala’in annobar, inda yanzu haka sojoji ke taimakawa jami’an lafiya raba magani.
Kotu ta tura mutum biyar gidan yari a Edo kan laifin zamba ta intanet
Haka ma malaman makaranta da dalibai likitoci na taimakawa wurin gano wadanda suka yi hulda da masu ɗauke da cutar.
Koriya ta Kudu mai makwabtaka ta ce har yanzu tana jiran amsa daga makwaciyartakan shirinta na taimakawa.
