Iran ta ce babu wani sabon ci gaba a tattaunawar sasanci da take da Saudiyya bayan rahotannin da ke cewa ministocin harakokin wajen ƙasashen biyu za su gana.
Badakalar N287m: EFCC Ta Tsare Tsohuwar Shugabar Majalisar Wakilai, Patricia Etteh
Kamfanin dillacin labaran IRNA ya ambato ministan harakokin wajen Iran Saeed Khatibzadeh ya ce babu wani ci gaba a tattaunawar da suka yi ta karshe.
Ya ce an tattauna a Bagadaza a ranar 21 ga watan Afrilu yadda za a ci gaba da tattaunawar.
Tun a bara Iraƙi ke jagorantar tattaunawa tsakanin Iran da Saudiyya waɗanda suka daɗe suna tsama tsakaninsu
