News
An Haramta Acaba A Wasu Sassan Birnin Legas ‘Har Abada’
Daga Maryam basiru fulatan
Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da haramta sana’ar acaba a Kananan Hukumomi shida na Jihar har abada.
Gwamnan ya sanar da haramcin ne bayan taron da ya yi da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a Jihar a ranar Laraba.
Kwankwaso ya fitar da sunayen ƴan takararar NNPP na maslaha a Kano
Babajide ya a ce haramcin ya shafi Kanana Hukumomin Ikeja da Surulere xa Eti-Osa da Lagos Mainland da Lagos Island da kuma Apapa.
Ya ce haramci ne na har abada, inda ya bukaci ’yan sanda su tabbatar ana bin umarnin yadda ya kamata.
Daukar matakin dai ba ya rasa nasaba da kisan wani matashin mawaki da ake zargin ’yan acaba sun yi inda suka kone gawarsa saboda wata takaddama kan Naira 100 a ranar Alhamis din da ta gabata.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
