Connect with us

News

ASUU: Daliban Najeriya sun yi barazanar rufe manyan filayen jiragen sama

Published

on

Daga Sulaiman ado Ahmad 

 

 

Ƙungiyar Ɗalibai ta Ƙasa, NANS, Shiyyar D, a yau Litinin ta yi barazanar rufe manyan filayen jiragen sama idan har aka ci gaba da jayayya tsakanin Ƙungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU da gwamnatin tarayya.

Hukumar EFCC ta sake gurfanar da Dasuki, Bafarawa, Yuguda, bisa zargin karkatar da kudi Naira Billiyan 388

Ko’odinetan NANS shiyyar Kudu-maso-Yamma, Adegboye Olatunji ne ya bayyana haka a Abuja yau Litinin, a wata zanga-zanga da su ka yi a sakateriyar jam’iyyar APC, ta nuna goyon bayan Gwamna Dapo Abiodun na Ogun domin ya tsaya takara karo na biyu.

Advertisement

Olatunji ya ce lokaci ya yi da bangarorin biyu za su hadu domin warware matsalolin da suka haddasa yajin aikin saboda dalibai ne ke illatuwa da hakan.

“Muna shirin mu toshe ma’aikatun gwamnati da ke samar mata kudi idan har ba a warware matsalar ASUU ba.

“Mun yi zanga-zanga a kan wannan batu ta hanyar mamaye manyan tituna a yankin Kudu-maso-Yamma amma muna ganin idan muka rufe filayen jiragen sama, gwamnati za ta yi wani abu game da yajin aikin,” inji shi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending