News
Cutar ƙyanda ta kashe yara 14 a Anambra
Daga yasir sani Abdullah
Gwamnatin Anambra ta tabbatar da mutuwar yara 14 sakamakon ɓarkewar cutar ƙyanda a ƙananan hukumomi tara na jihar.
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kwankwaso, da wasu 3 sun fice daga NNPP zuwa APC
Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Afam Obidike ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai kan yaƙi da cutar kyanda a Awka a yau Laraba.
Ya ce an samu sabbin kamuwa da cutar ƙyanda sama da 414 a kananan hukumomi tara na jihar ba.
Obidike ya lissafa kananan hukumomin da abin ya shafa da suka hada da Anambra ta Gabas, Anambra ta Yamma, Ayamelum, Ihiala, Idemili North, Nnewi North, Onitsha North, Njikoka, da Oyi.
Kwamishinan ya bayyana cewa tallafin Hukumar Lafiya ta Duniya da Asusun Tallafawa Yara na Majalisar Dinkin Duniya ya taimaka wa jihar wajen daƙile yaɗuwar cutar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
