Connect with us

News

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kwankwaso, da wasu 3 sun fice daga NNPP zuwa APC

Published

on

Daga yasir sani Abdullah 

 

 
 
 

Dan majalisar dokokin jihar Kano mai wakiltar mazabar Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Madobi, Kabiru Yusuf Isma’il ya sauya sheka daga jam’iyyar New Nigerian People’s Party (NNPP) zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Kano.

 

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar ta bayyana cewa dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Dawakin kudu, Mu’azzam El-Yakubu, shi ma ya fice daga jam’iyyar NNPP ta Kwankwaso zuwa APC.

Rashan Cika Alkawari Yazama Dabi,ar Matasa Da Kuma Jagororin Al,umma-Kabiru Basiru Fulatan

 

Yace a kwanakin baya guguwar sauya sheka ta mamaye jam’iyyar NNPP, musamman ‘yan majalisar jiha da na kasa.

 

Malam Garba yace tuni dan majalisar dokokin jihar mai wakiltar Bagwai da Shanono, Isa Ali ya koma jam’iyyar APC kwanaki bayan ya koma jam’iyyar NNPP.

Advertisement
 

Abokin aikin Garba a majalisar Jaha mai wakiltar mazabar Dambatta, Murtala Kore ya kuma fice daga jam’iyyar NNPP ya ci gaba da zama a jam’iyyar APC.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending