Connect with us

News

Yanzu yanzu: Ƙungiyar Malaman Kwalejin Fasaha ta ƙasa (ASUP) ta bada sanarwar janye yajin aikin

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

Ƙungiyar Malaman Kwalejin Fasaha ta ƙasa (ASUP) ta bada sanarwar janye yajin aikin gargadin da ta shiga makwanni biyu da suka wuce sannan kuma ta umarci ƴaƴan kungiyar nata da su dawo bakin aiki a ranar Litinin mai zuwa 30 ga watan Mayu, na shekarar 2022.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Ƙungiyar Shamma S. Kpanja ya fitar a safiyar yau Asabar.

Advertisement

Majiyar mu ta tuntubi shugaban ƙungiyar reshen Kano State Polytechnic Dakta Muntaka Dahiru inda ya tabbatar mana da maganar komawar a ranar Litinin mai zuwa 30 ga watan Mayun.

Ƙungiyar ta kara da cewa ƴaƴan kungiyar nata su saurari umarni na gaba don gane da yajin aikin bayan babban taro na 103 da Ƙungiyar za ta gabatar a watan Yuni.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending