News
Wani lauya ya maka gwamnan kano Kara a gaba kotu
Daga Yasir sani Abdullahi
Wani lauya Mai zaman kansa ya maka gwamnan kano DR Abdullahi Umar ganduje a gaban kotu
Voice of America ( voa) ta rawaito cewa lauyan ya maka gwamnan kano a gaban babbar kotun jahar kano bisa tuhumar gwamnan da Hana ja,ma,a fitowa a ranar asabar din karshe mako
Louyan ya Kara da cewa Gwamnatin tana Hana Jama,a fitowane karfe 7 na safe sai zuwa karfe 10 na safiyar karshen makon kowane watan a ranar asabar
KANO, NIGERIA —
Tun shekarun zamanin mulkin soja ne dai gwamnatin ta kebe wadannan sa’o’i guda uku, inda ake hana zirga zirgar mutane a birni da kewayen Kano domin Jama’a su gudanar da aikin shara da tsaftace muhallin su.
Kamar yadda takardar karar da lauyan Barrister Ibrahim Baba ya gabatarwa kotun ta nuna wadanda ake kara sune gwamnan na Kano da kwamishinan ‘yan sanda na Kano da kwamishinan shari’a kuma Atoni Janar na Kano da kwamishinan Muhalli kana da ma’aikatar muhalli ta Kano.
Barr. Ibrahim Baba wanda ya yi karin haske game da kunshin karar yace hana mutane zirga zirga a cikin wadannan sa’o’i sun tauye hakkin sa a matsayin na dan jihar Kano da sauran mutane mazauna jihar Kano, yana mai cewa matakin ya ci karo da tanade tanaden ‘yancin walwala da kundin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa ‘yan kasa da kuma daftarin kare hakkin dan adam na nahiyar Afrika.
A cewar Barr Ibrahim Baba, akwai banbanci tsakanin tsaftar muhalli da haramta zirga zirga Jama’a a gari.
Yanzu dai abin jira a gani shine yadda zata kaya a gaban babbar kotun ta Kano.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
