Connect with us

News

Tsohon Ministan Harkokin Ƙasashen Waje ya samu tikitin takarar Sanatan Jigawa a PDP

Published

on

Daga khadija Abdullah muhmd 

 

 

Tsohon Ministan ƙasa a Ma’aikatar Harkokin Ƙasashen Waje, Dakta Nuruddeen Muhammad ya yi nasarar lashe zaben fidda-gwani na takarar sanatan Jigawa ta Gabas a jama’iyyar PDP.

XASUU Ta Yi Watsi Da Tayin Tallafi Don Ta Janye Yajin Aiki

Tsohon Ministan, wanda kuma ya taɓa kula da Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta tarayya ya lashe zaben ne babu hammayya, a wani zaɓen cikin gida na musamman da aka yi a jiya Alhamis a garin Hadejia, da ke jigawa.

Advertisement

Da ya ke jawabin amincewa, ɗan takarar ya godewa dukkanin wakilan jama’iyya da su ka zaɓe shi, inda ya suffanta hakan da karramawa da su ka yi masa.

Ya kuma jawo hankalin al’umma ma su zaɓe da su kaɗa ƙuri’arsu a kakar zaɓe mai zuwa a kan doron tunanin matsalolin da su ke addabarsu.

Ya lissafo matsalolin kamar haka; ambaliyar ruwa, kwararowar hamada, yasar kogin Hadeja da kuma yawaitar ciwon k’oda da dai sauransu, inda ya ci alwashin magance su.

Daily Nigerian Hausa ta tuna cewa Muhammad shine wadda yayi wa jama’iyyar PDP takarar mataimakin gwamna a kakar zaben 2015.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending