News
Ina da fatan samun nasara, don haka bazan janyewa Atiku ko Tinubu ba — Kwankwaso
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Tsohon gwamnan jihar Kano, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, yace yana da kyakykyawan fatan samun nasara a babban zaben shekarar 2023 mai zuwa, don haka bazai janyewa dan takarar PDP Atiku Abubakar ko kuma APC Bola Ahmed Tinubu da sauransu ba, musamman ma yakinin da yake dashi akan gyaran dokar zaɓe, wacce yace abu mai wahala ayi masa murdiya, domin dai talakawa suna matukar fata a gare shi.
Kwankwaso ya bayyana haka ne cikin wata tattaunawa da jaridar Punch, inda yace matukar zaɓe za’ai na tsakani da Allah, to zaiyi wahala su fadi zaɓe, domin akwai muradin talakawa a tare dashi, bisa burinsu na inganta harkokin ilimi, tsaro, hada kan al’umma, da sauran ayyuka na inganta rayuwa a karkashin jam’iyyarsu ta NNPP mai alamar kayan marmari.
“Ba ni da jam’iyyata ne zamu kayar da wadancan yan takara ba, jam’iyya alama ce, talakawa ne zasu fita suyi zaɓe, kuma sun san bambamcin da yake tsakaninmu dasu, domin basu da abinda zasu fadawa mutane don a zaɓe su, sabanin ni da nayi ayyuka na al’umma a baya, an ga irin rawar dana taka.”
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
