News
Za mu murƙushe masu yi wa tsaron Najeriya zagon-ƙasa – Buhari
Daga Muhammad Muhammad Ibrahim
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya shaida cewa masu daukar doka a hannusu, mallakar makamai ta haramtacciyar hanya, da kuma ribauta daga jefa tsoro da matsalolin tsaro za su ɗanɗana kudarsu.
Shugaban na waɗannan kalamai ne a garin Wudil na jihar Kano, a bikin yaye ɗalibai ‘yan sanda da ya halarta.
Buhari ya ce gwamnatinsa, za ta ci gaba da yaƙi da munanan aƙidu da miyagun mutane, yana mai jan hankali ‘yan sanda kan mayar da hankali a ayyukansu.
Sannan ya jadada bukatar samar da ci gaba a fasaha ko kariya daga hare-haren intanet, sannan ya ce za a tarwatsa maƙiyan kasa.
Najeriya dai na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro, da sace mutane domin neman kuɗin fansa.
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News4 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News21 hours ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
