Connect with us

News

Gwamnan Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri’arsa

Published

on

Daga Kabiru basiru fulatan

Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri’arsa a zaben da ake gudanarwa a jihar.

Mista Fayemi ya kaɗa ƙuri’ar tasa ne a rumfar zaɓensa da ke mazaɓa ta 11 a Isan-Ekiti. Ita ma matarsa ta kaɗa ƙuri’arta ba tare da wata matsala ba.

Mista Fayemi ya yi kira ga waɗanda suka cancanci jefa ƙuri’a da su yi abin da ya dace wurin zaɓen wanda suke so ya jagorance su.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ba jami’an tsaro haɗin kai domin ganin an gudanar da zaɓen lafiya an kuma gama lafiya.

Gwamna Fayemi dai zai miƙa ragamar jagorancin Jihar Ekiti ga duk wanda ya yi nasara a wannan zaɓe.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending