News
Gwamnan Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri’arsa
Daga Kabiru basiru fulatan
Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri’arsa a zaben da ake gudanarwa a jihar.
Mista Fayemi ya kaɗa ƙuri’ar tasa ne a rumfar zaɓensa da ke mazaɓa ta 11 a Isan-Ekiti. Ita ma matarsa ta kaɗa ƙuri’arta ba tare da wata matsala ba.
Mista Fayemi ya yi kira ga waɗanda suka cancanci jefa ƙuri’a da su yi abin da ya dace wurin zaɓen wanda suke so ya jagorance su.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ba jami’an tsaro haɗin kai domin ganin an gudanar da zaɓen lafiya an kuma gama lafiya.
Gwamna Fayemi dai zai miƙa ragamar jagorancin Jihar Ekiti ga duk wanda ya yi nasara a wannan zaɓe.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
