News
Gwamnan Zamfara Matawalle ya bai wa ma’aikata hutun mako ɗaya don su yi rajistar zaɓe
Daga yasir sani abdullahi
Gwamnatin Jihar Zamfara a arewacin Najeriya ta bai wa ma’aikatan jihar hutun mako ɗaya domin su yi rajistar katin zaɓe da ake gudanarwa yanzu haka a faɗin ƙasar.
Ɗan damfara da yaudara a facebook, wanda ke nuna kansa a matsayin Zahra Mansur ya shiga hannu
Matakin na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamashinan Yaɗa Labarai na Zamfara Ibrahim Dosara ya fitar a yau Asabar.
Ya ce Gwamna Bello Matawalle ya amince da ba da hutun ne daga Litinin, 20 zuwa 24 ga watan Yuni.
“Sakamakon wannan sanarwa, an umarci dukkan kwamashinoni da masu bai wa gwamna shawara da sakatarori da sauran ma’aikatan gwamnati da jami’an jam’iyyun siyasa da su saka ido kan yadda aikin rajistar ke tafiya,” a cewar kwamashinan.
Ƙungiyoyi da ‘yan gwagwarmaya a Najeriya na ci gaba da kira ga hukumar zaɓe ta ƙasa INEC da ta tsawaita wa’adin yin rajistar, suna masu cewa mutane da dama ba su samu damar yi ba saboda ƙarancin kayan aiki da kuma cunkoso.
INEC ta saka ranar 30 ga watan Yuni a matsayin ranar ƙarshe da za a rufe aikin rajistar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
