News
Gwamnatin Kano ta zabi kamfanin jirgin sama daya tilo, don jigilan alhazan jihar
Daga Muslim yunus Abdullahi
Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da cewa jirgin Max Air ne zai yi jigilar Alhazanta zuwa kasa mai tsarki a bana.
Shekara da shekaru suna aiki da kamfanin Max Alr kuma bai taba basu matsala ba, don haka a bana ma da shi zasu yi
Gwamnan Zamfara Matawalle ya bai wa ma’aikata hutun mako ɗaya don su yi rajistar zaɓe
Babban sakataren hukumar Jin dadin Alhazai na Kano Muhammad Abba Dambatta ne ya tabbatar da hakan yayin taron manema Labarai yau Lahadi.
Ya ce bayan dogon nazari da tattaunawa da masu ruwa da tsaki yanzu an tabbatar da Jirgin Max Air a matsayin wanda zai yi jigilar alhazan Kano, duk da tarin kamfanonin da suka nemi makamanciyar wannan dama.
Idan za a iya tunawa a makon da ya gabata ne dai Kamfanin Azman Air ya ce hukumar jin dadin alhazai ta kasa NAHCON ta bashi damar ya yi jigilar Alhazan Kano.
Sai dai hukumar Jin dadin Alhazai ta Kano ta ki amincewa da baiwa Kamfanin dama.
Duk kuwa da cewa kamfanin mallakin dan Kano ne, kuma da dama cikin Ma’aikatan kamfanin yan Kano ne.
Inda ta ce Shekara da shekaru ta na aiki ne da Kamfanin Max Air kuma bai taba Basu matsala ba, babu dalilin da zai sa su yi watsi da shi.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
