News
Ɗumbin jama’a na ‘tserewa’ daga garin Mada na Zamfara bayan harin ƴan bindiga
Daga Kabiru basiru fulatan
Bayanai daga garin Mada na Jihar Zamfara na cewa mutane na tserewa daga garin bayan harin da ‘yan bindiga suka kai a jiya.
Shaidu sun tabbatar wa BBC cewa ƴan bindigan sun harbi mutum ɗaya sannan suka tafi da wasu mutum huɗu baya ga ɗumbin dabbobi da suka kora.
Sai dai shaidun sun ce sojoji na dakatar da mutane da ke tserewa domin barin garin, inda suke hana su ficewa, lamarin da ya jawo mazauna Mada ke zanga-zanga.
BBC ta ce ta tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ta Zamfara domin ji daga gare shi, amma bai amsa kiran wayar ba.
Wannan hari dai, shi ne irinsa na uku a cikin kwana uku a jere da ƴan bindiga ke kaiwa garin na Mada da wasu garuruwan makwabta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
