Connect with us

News

Tsananin Yunwa, Hawan Jini Da Damuwa Sun Hallaka Yan gudun Hijira 23 A Katsina

Published

on

Buhari

Daga khadija Abdullah muhmd 

 

Advertisement

 

A gefe guda kuma, wani lamari mai tayar da hankali kamar yadda Salisu ya bayyana, shi ne yadda akasarin yaran da ke garin da kuma na sansanin ba sa iya samun ilimi

Advertisement

Kasuwar yan kwallo: Makomar Raphinha,Skriniar, Zinchenko, Richarlison, Eriksen, de Jong da Pereira

Kimanin mutane Ashirin da uku ne suka rasa rayukan a sanadiyar yunwa, hawan jini, damuwa a sansanin ‘yan gudun dake karamar hukumar Jibiya ta jiharKatsina.

Advertisement

 

Shugaban Sansanin sa’ad Salisu ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai jiya a karamar hukumar ta Jibiya.

Advertisement

 

Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, A wani rahoto da kungiyar cigaban karamar hukumar Jibiya ta fitar na ranar Litinin, ya nuna cewa, akalla ‘yan gudun hijira dubu ashirin da biyu, da dari uku da sittin da biyar (22,365) daga yankunan Shimfida, Garin Maiwuya, Garin Zango, Garin Kwari da kauyukan Tsambaye suna zaune ne cikin garin Jibiya.

Advertisement

 

Yan gudun hijirar na samun mafaka ne a makarantar sakandiren ‘yan mata ta gwamnati da ke Jibiya.

Advertisement

 

Kazalika Shugaban sansanin ‘yan gudun hijirar, Sa’ad Salisu, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar ci gaban matasa na garin Shimfida, ya bayyana cewa akalla mata 35 ne suka haihu a sansanin a cikin watanni hudu da suka gabata, yana mai cewa adadin zai iya zarce haka, nan gaba kadan.

Advertisement

 

A gefe guda kuma, wani lamari mai tayar da hankali kamar yadda Salisu ya bayyana, shi ne yadda akasarin yaran da ke garin da kuma na sansanin ba sa iya samun ilimi.

Advertisement

 

Ya Kuma Kara da cewa, akwai yara sama da dubu uku (3,000) a sansanin da suka bar yankunan su da suke kuma zuwa makaranta amma yanzu ba sa iya zuwa makarantar, saboda gwamnati ba ta tanadar musu da makaranta ba a sansanin da suke zaune.

Advertisement

 

Sai dai Salisu ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta daukar matakin maido da tsaro a cikin yankunan da harin yan bjndiga ya dai-daita, domin su koam su cigaba da ayyukan noma.

Advertisement

 

A nasa jawabin shugaban karamar hukumar Jibiya, Bishir Sabi’u ya ce gwamnati ta samar da isassun kayan agaji ga ‘yan gudun hijirar.

Advertisement

 

Sai dai Kuma a cewarsa, a kullum ana dafa musu buhunan shinkafa guda goma sha biyar, domin ciyar da yan gudun hijiran da ke zaune a sansanin.

Advertisement

 

Kana ya bayyana cewa, gwamnatinsa tana baiwa ‘yan gudun hijirar dubu dari biyu N200,000 duk mako don tallafa musu wajen gudanar da ayyukansu na yau da kullun a sansanin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending