News
Ma’aikatar lafiya ta tabbatar da ɓullar Kwalara a Kano
Daga khadija Abdullah muhmd
Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta tabbatar da ɓullar cutar amai da gudawa a birnin Kano.
Babban jami’in kula da cututtuka masu yaɗuwa na ma’aikatar Sulaiman Iliyasu ne ya tabbatar da hakan a zantawarsa da Wakiliyar Freedom Radio Safara’u Tijjani Adam ta wayar tarho.
Ya ce an samu rahoton ɓullar cutar a ƙaramar hukumar Ɗanbatta wadda har aka samu asarar rayukan mutane biyu.
“A watan Afrilu mun samu rahoton ɓullar cutar amai da gudawa a Ɗanbatta wadda daga nan kuma sai cutar ta ɓulla a ƙaramar hukumar Gwarzo”.
Dr. Iliyasu ya ci gaba da cewa “Ya zuwa yanzu sama da mutane 25 zuwa 30 ne suka kamu da cutar a ƙwaryar birnin Kano kamar yadda sakamakon gwajin da muka yi ya tabbatar”.
A cewar jami’in a yanzu haka ƙananan hukumomin da suka samu ɓullar cutar sun haɗa da: karamar hukumar Dala da Ungoggo ƙaramar hukumar birni sai kuma Tarauni.
Dr. Sulaiman Isyaku ya buƙaci al’umma da su ƙara kula da tsaftar muhallansu da kuma kai rahoton duk wata cuta da ta ɓulla ga hukumomin lafiya don ɗaukan matakin gaggawa
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
