An saka dokar hana fitar dare a wasu garuruwa biyu na kasar Sudan, bayan artabu na tsawon kwanaki tsakanin wasu kabilu wanda ya jawo mutuwar aƙalla mutum 31 da jikkata gwammai.
An aike da sojoji zuwa yankin domin kwantar da tarzomar da ta ɓarke kan rikicin filaye tsakanin kabilun Berti da kuma Hausawan da ke kudu maso gabashin Jihar Blue Nile.
Ma’aikacin Filin Jirgi Ya Saci Jirgin Sama
Rikicin ya ɗaiɗaita gwamman mutane da kuma sanadin ƙona shaguna da dama yayin artabun da aka soma tun ranar Litinin.
Duk da sanya dokar hana fitar daren, rahotanni na nuna cewa ana ci gaba da gwabza fada a daya daga cikin garuruwan mai suna Roseires .
Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a Sudan, ya kira ga al’ummomin da su kai zuciya nesa.
. Source bbc
