News
Kenya za ta hukunta duk wanda ya ki sayar da masara a farashin gwamnati
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Kenya ta ce za ta kama tare da hukunta duk wanda aka samu yana sayar da fakitin garin masara mai nauyin kilogiram 2 a sama da farashin sulai (shillings) 100 da aka kayyade.
A wani jawabi da ya yi ta talabijin a yau Alhamis Shugaba Uhuru Kenyatta ya jaddada umarnin da gwamnatinsa ta bayar na zaftare farashin da sama da rabin kudin da ake sayar da garin masarar a da sulai 205.
Zargin kalaman ɓatanci: A canja alƙalin da ke yin shari’a ta — Abduljabbar
Kakakin gwamnatin, Cyrus Oguna, ya gaya wa BBC cewa ana duba yadda za a biya ‘yan kasuwar da suka riga suka sayo masarar da tsada kafin a bayar da sanarwar rage farashin.
Wasu ‘yan kasuwar masu shaguna ba su fara sayar da masarar a sabon farashin da gwamnati ta tsayar ba saboda tsoron kada su yi asara.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
