News
Muna ƙarancin wurin ajiye tubabbun ‘yan Boko Haram – Sojin Najeriya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumomi a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, sun ce sun fara rasa wuraren da za su ajiye mayaƙan Boko Haram da suka miƙa wuya.
Babban jami’in soja Manjo Janar Chris Musa ya ce a yayin da miƙa wuyan da mayaƙan Boko Haram ɗin ke yi yake taimakawa wajen shawo kan rikicin da ya addabi yankin, a gefe guda kuma babu isassun wuraren ajiye su.
Gwamnatin Tarayya Za Ta Kashe N30bn Don Gyaran Majalisa
Babban janar ɗin ya ce zuwa yanzu akwai mayaƙan da suka yi saranda kuma suke jiran bin matakan sauya musu tunani, amma ba su da wajen ajiye su.
Wuraren ajiye mutanen sun cika maƙil – kuma a yanzu hukumomi suna duba yiwuwar gina wasu.
Matakan sauyawa da gyara tunani na cikin ƙoƙarin da gwamnatin Najeriya ke yi don kawo ƙarshen ayyukan masu iƙirarin jihadi, musamman a arewa maso gabashin ƙasar.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi ƙiyasin cewa kusan mutum 350,000 ne suka mutu a rikici tsakanin ƙungiyar Boko Haram da rundunar sojin ƙasar cikin shekara 12. Amma adadin ka iya fin haka.
Janar Chris Musa ya ce wani babban ƙalubalen shi ne yadda suke samun matsalar mayar da ƴan gudun hijira matsugunansu.
Hakan na faruwa ne sakamakon ƴan tayar da ƙayar bayan sun daddasa nakiyoyi a kan hanya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
