Connect with us

News

Jihohin Legas da Kano ne kan gaba a yawan sabbin masu rajistar zabe – INEC

Published

on

Daga muhammad muhammad zahraddin

 

 

 

Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya ta ce an samu sabbin masu rajistar zabe sama da miliyan 11 da suka yi rajistar a fadin kasar.

 

Advertisement

Alkaluman da hukumar ta fitar a shafinta na Tuwita sun nuna cewa mutum miliyan 11,011,119 ne suka kammala rajistar a lokacin da ta wallafa sakon.

Dawowar Messi zuwa Barcelona ba abu ne mai yiwuwa ba yanzu

Alkaluman sun kuma nuna cewa jihar Legas ce kan gaba a yawan wadanda suka yi rajistar, inda take da mutum 508,936, sai kuma jihar Kano da aka samu sabbin masu rajistar zaben 500,207, sai Delta mai 481,929, sai kuma jihohin Rivers da Kaduna da ke matsayi na hudu da na biyar

 

Alkaluman sun kuma nuna cewa matasa ne masu shekaru tsakanin 18 zuwa 34, suka fi yin rajistar zaben

 

Advertisement

Sannan kuma alkaluman sun nuna cewa mata sun fi maza yin rajistar, inda aka samu mata miliyan 5,558,048, fiye da adadin maza miliyan 5,453,071 da suka yi rajistar.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending