News
Sarkin Kano ya sabunta lasisinsa na tuƙi
Daga maryam Abdullahi muhmd
Mai martaba Sarkin Kano, Dakta Aminu Ado Bayero, ya sabunta lasisin tuki a hukumar kiyaye haɗurra ta kasa FRSC, a babbar cibiyar bada lasisin tuki da ke Hukumar Tattara Haraji ta Jihar Kano.
Sarkin ya samu lasisin sa na farko a shekarar 1982, kamar yadda wata sanarwa da FRSC ga fitar a yau Talata .
Najeriya Ce Ta 18 A Gasar Tsere Da Tsalle-Tsalle Ta Duniya
Sanarwar ta fito ne daga bakin Kwamandan hukumar FRSC reshen jihar Kano, CC Zubairu Mato, a Kano.
Sanarwar ta ce bayan ziyarar ban girma da Sarkin ya kawo; akwai bukatar sarakunan gargajiya su kwadaitar da talakawansu wajen aiwatar da lasisi.
“Aikin yi lasisin abu ne mai kyau kuma kyakkyawan misali, ne” in ji shi.
Hakanan ya nuna mahimmancin samun lasisin saboda yana iya zama katin shaida na mutum.
Tun da fari, Sarki Aminu ya ja hankalin jama’a da su rika tuka ababen hawa, babura masu ƙafa uku da aka fi sani da Keke Napep da babura da su yi lasisin su tare da sabunta su idan sun ƙare.
Ya kuma buƙaci sauran sarakinan gargajiya da su nuna alamar shugabanci su fito da kansu domin sabunta lasisi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
