Connect with us

News

Mutum 18 sun mutu a arangama tsakanin ‘yan bindiga da jami’an sa-kai a Filato’

Published

on

Yan bindiga

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

 

Mutum 16 da ake zargin ‘yan bindiga ne da ‘yan vigilante biyu sun mutu a bata-kashi tsakanin bangarorin biyu a garin Bangalala da ke karamar hukumar Wase a Jihar Filato.

Bangalala na da nisan kilomita 100 daga garin Wase, hedikwatar karamar hukumar.

Mukaddashin firaministan Iraƙi ya roƙi masu zanga-zanga su kwantar da hankulansu

Advertisement

Kauyukan da ke Wase na fama da hare-haren ‘yan bindiga, satar mutane da shanu, abin da ya tilastawa mutane da dama tserewa daga gidajensu.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru a kokarin jami’an sa-kai na vigilante kwato kauyen Bangalala da ke hannun ‘yan bindiga tsawon watanni.

Mazaunan yankunan dai sun tabbatar da wannan al’amari, sai dai jami’an tsaro ba su tsokaci ba kawo yanzu.

Bbc Hausa

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending