Connect with us

News

Ƴan fashin daji na ta kwararowa jiha ta, Gwamnan Nassarawa ya koka

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

 

 

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana damuwa game da yadda gungun ‘yan fashin daji ke tururuwa zuwa jiharsa bayan koro su daga maƙwabtan jihohi.

BBC ta rawaito cewa, Gwamna ya ce jami’an tsaro sun lura da ƙaruwar ‘yan bindiga a ƙaramar hukumar Karu, wadda ke da nisan ƙasa da kilomita 30 daga Abuja babban birnin ƙasar.

Advertisement

An kama mutanen hudu da ake zargin sun taimaka wajen kai hari gidan yarin Kuje

“Mun lura da tarin ‘yan fashin nan da aka koro daga jihohin Kaduna da Katsina da Neja da Kebbi musamman a yankunan Rugan Juli da Rugan Madaki da ke Ƙaramar Hukumar Karu,” a cewar gwamnan yayin taron manema labarai ranar Asabar.

“Kazalika, mun ga wasu daga cikinsu a ƙananan hukumomin Wamba da Toto.”

Haka nan gwamnan ya ce sun yi nasarar kama wasu daga cikin fursunonin da suka tsere daga Gidan Yari na Kuje a Abuja bayan mayaƙan Boko Haram sun fasa shi a watan Yuni.

Wasu mazauna yankunan da Gwamna Sule yake magana sun faɗa wa BBC Hausa cewa sun shaida ƙaruwar satar mutane a yankunan nasu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending