Connect with us

News

Sarkin Musulmai ya gaya wa masu hidimar ƙasa cewa Shari’ar Musulunci Musulmai kawai ta shafa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Sarkin Musulmai, Alhaji Muhammad Abubakar ya tabbatar wa masu yi wa ƙasa hidima a Sokoto cewa ba za a yi amfani da dokokin Shari’ar Musulunci ga waɗanda ba Musulmai ba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Sultan Sa’ad ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis a fadarsa, a lokacin da masu kula da harkokin ƴan bautar kasa karkashin jagorancin shugabansu suka kai masa ziyarar ban girma.

Advertisement

Tsawa ta faɗo tare da raunata mutum hudu a kusa da Fadar White House ta Amurka

Ya kuma tabbatar musu cewa za su samu tsaro duk da cewa akwai kalubale na tsaro a kasar baki daya.

Advertisement

Abubakar ya kara cewa za a kyale su su gudanar da addinansu.

Ya bayyana cewa ba za a dora wa wadanda ba Musulmi ba hukuncin Shari’ar Musulunci, kuma ya jaddada cewa babu wanda za a tursasa wa shiga Musulunci ba da son ransa ba.

Advertisement

“A Sakkwato, Shari’ar Musulunci ta sauka ne kawai a kan Musulmai, babu wanda zai tursasa masa saka hijabi, ko bin Shari’ar Musulunci idan ba Musulmi ba ne,” ya bayyana.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending