Connect with us

News

An kashe ‘yansanda da Indiyawa a wani harin bindiga a Kogi

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ‘yan bindiga sun kashe mutum shida a wani harin da suka kai kan motar Bas a jihar Kogi da ke arewa maso tsakiyar Najeriya.,

Mutanen da aka kashe sun haɗa da Indiyawa biyu da ke aiki a wani kamfanin gine-gine, da ‘yan sanda biyu da ke basu kariya da direbansu mutum biyu a harin na ranar Juma’a.

An kai harin ne a yankin Ajaokuta.

Ko a watan da ya gabata sai da ‘yan bindiga suka kashe ‘yan sanda uku da masu aikin sa-kai biyar a wani hari ba-zata da suka kai a jihar.

A watan Yuni da Yuli ma sai da mayakan jihadi na IS suka hallaka ‘yan sanda hudu a hari kan ofisoshinsu biyu a yankin Okehi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending